Lokuta 14 Masu Muhimmanci Da Ake Karɓar Addu’a

Don Allah ko ba zaka karanta ba katura wa yan uwa saboda Al’umma su Amfana da kai.

Kowanne lokaci idan mutum yayi addu’a Allah yana karba. Sai dai Ubangiji cikin baiwarsa da falalarsa ya ke’banci wasu lokuta ya sanya musu albarka da baiwa fiye da sauran lokutai.

Wadannan lokutan sun hada da:

1. DAREN JUMA’A: Wato ranar
alhamis da dare, da kuma
wunin jumu’ar. Ma’aikin Allah
(alaihis salam) yace “babu wani
bawa wanda zai dace yana addu’a acikinta fache sai Allah
ya amsa masa”. 

2. WATAN RAMADHAN: gaba
dayansa lokaci ne na amsar
addu’a.

3. LAILATUL QADARI: Shima
lokacin amsar addu’a ne. 

4. TSAKAR DARE: Musamman ma sulusin karshensa.. Lokaci ne da Allah yake gwanjon rahamarsa ga bayinsa. 

5. LOKACIN DA AKE KIRAN
SALLAH, DA KUMA TSAKANIN
KIRAN SALLAH DA TADA IQAMAH


6. LOKACIN DA AKA IDAR DA
SALLOLIN FARILLAH
.

7. LOKACIN DA AKA GAMA
KARATUN ALQUR’ANI, KO
WA’AZI KO WATA KOYARWA TA
ILMI
: Shima lokacin karbar addu’a ne. 

8. LOKACIN DA ZAKARA YAYI CHARA. Shima lokacin amsar
addu’a ne. 

9. LOKACIN TAFIYA TA ALHERI:
kamar tafiya hajji, sada zumunci, jihadi, ko fatauci.
Shima lokacin amsar addu’a. 

10. RANAR ARFA: awannan
ranar, da wanda yake Makkah,
da wanda yake gida, duk Allah
yana amsar addu’arsu. 

11. LOKACIN ZUBAN RUWAN
SAMA
_ Shima ana amsar addu’a acikinsa. 

12. LOKACIN DA AKA TSAIDA
SAHUN YAQIN DAUKAKA
KALMAR ALLAH
. Shima ana
amsar addu’a cikinsa. 

13. LOKACIN DA MUTUM YAYI
SUJJADAH
. Shima ana amsar
addu’a cikinsa. 

14. LOKACIN DA MUTUM YA
FARKA DAGA BARCI
: musamman idan mutum ya karanta “sub’hanallah wal’hamdulillah, wa la’ilaha’illal-Lah wallahu akbar” (QAFA 10). Duk abinda ka roka Mustajabah.