Yan Uwan Juna: Duk Sun Mutu Wajen Yiwa Kasar Su Hidima

Yan uwa guda biyu wadanda sukayi jarumtaka duka sun rasa rayukan su suna yiwa kasar su hidima.

A jihar Katsina a shekarar 2019, Kaftin Jamilu Ali Hassan, karamin jami’i, ya yi sadaukarwa, wacce ta sanya ya rasa ran shi.

A jihar Delta a shekarar 2024, kwamandan rundunar Laftanar Kanar Ali Abdullahi Hassan ya biya farashi mai tsoka, bayan wasu matasa sun yi masa kisan gilla tare da wasu sojojin Najeriya 16.