Gwamnan jihar Jigawa Umar Namadi ya dakatar da kwamishinan kasuwanci na jihar Alhaji Aminu Kanta bisa zargin almubazzaranci da kudaden da aka ware domin yin ciyarwa a azumin watan Ramadan.
Sakataren gwamnatin jihar Malam Bala ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa DAILY POST.
Sanarwar ta ce an dakatar da kwamishinan ne bisa zargin karkatar da kudaden da aka ware domin shirin ciyarwa a jihar na karamar hukumar Babura.
A cewar sanarwar: “Dakatar ta fara aiki nan take har sai an yanke shawarar kwamitin binciken da gwamnan jihar ya kafa domin gudanar da bincike kan zargin.”
Idan dai za a iya tunawa Majalisar zartaswar jihar ta amince da fitar da Naira biliyan N2.8 don ciyarwa a azumin watan Ramadan a fadin kananan hukumomin jihar 27.