Badakalar Betta Edu: An Kwato Biliyan N30, Ana Binciken Asusun Banki 50 – EFCC

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati, EFCC, ta kwato Naira Biliyan 30 a binciken da take yi bayan dakatarwar da aka yiwa ministar harkokin jin kai da yaki da fatara, Betta Edu da tsohuwar Shugabar Hukumar Kula da Zuba Jari ta Kasa, NSIPA, Halima Shehu.

Hukumar da ke yaki da cin hanci da rashawa ta kuma bayyana cewa ta sanya asusu 50 na banki a binciken da ake yi.

Shugaba Bola Tinubu ya dakatar da Edu da Shehu kimanin watanni uku da suka gabata bisa zargin karkatar da kudade.

Shugaban ya kuma dakatar da shirin na Social Investment Program yayin da ya umurci hukumar EFCC da ta dauki nauyin lamarin tare da binciki dukkan jami’an da aka kama.

Ola Olukoyede, Shugaban EFCC ne ya bayyana hakan a cikin watan Maris na e-mujallar hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC-Alert.

Ya ce: “Muna da dokoki da ka’idoji da ke jagorantar binciken mu. ‘Yan Najeriya kuma za su san cewa an riga an dakatar da su kuma wannan ya dogara ne akan batun binciken da muka yi, kuma shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa a shirye yake ya yaki cin hanci da rashawa.

“Bugu da kari, dangane da wannan lamari, mun kwato sama da Naira biliyan 30, wadanda tuni ke cikin asusun gwamnatin tarayya. Yana ɗaukar lokaci don kammala bincike; mun fara wannan lamari ne kasa da makonni shida da suka gabata.

“Akwai kararrakin da ake daukar shekaru ana bincike. Akwai kusurwoyi da yawa a gare shi. Kuma muna bukatar mu bi diddigin wasu binciken da muka gani. Ya kamata ‘yan Nijeriya su ba mu lokaci kan wannan al’amari; muna da ƙwararru akan wannan harka kuma suna buƙatar yin abubuwa daidai. Akwai jagora da yawa nan da can.

“Kamar yadda yake a yanzu, muna binciken sama da asusun banki 50 da muka gano kudaden a ciki. Wannan ba wasan yara ba ne. Wannan babban al’amari ne. Sai ku yi tambaya game da ƙarfin ma’aikatana. Kuma a sake, muna da dubban sauran shari’o’in da muke aiki akai. “