Tinubu Zai Kaddamar Da Tsarin Bai Wa Dalibai Rancen Kudi

Fadar shugaban kasa ta bayyana cewa a ranar Alhamis ne shugaban kasa Bola Tinubu zai kaddamar da shirin bayar da lamuni ga dalibai.

Mai ba Tinubu shawara na musamman kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, Ajuri Ngelale, ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi yayin da ya bayyana a shirin gidan talabijin na TVC.

A cewar Ngelale, “A cikin makon nan mai zuwa, a ranar Alhamis, shugaban kasar zai kaddamar da shirin bayar da lamuni ga dalibai na kasa mai dimbin tarihi.

“Wannan wani babban nau’i ne na rage wa ‘yan Najeriya da iyalai da matasa a daidai lokacin da ‘yan Najeriya ke cikin kunci. Mun yi imanin wannan ita ce hanyar da za a bi. “

A ranar 12 ga Yuni, 2023, Tinubu ya sanya hannu kan dokar samun damar zuwa manyan makarantu, 2023, ta zama doka.

Kudirin yana nufin baiwa ɗalibai damar samun lamuni marasa riba don dalilai na ilimi.

Gwamnatin tarayya ta jinkirta fara shirin wanda aka shirya fara farawa tsakanin Satumba da Oktoba 2023.