Addini

Tarihin Annabi Isma’il Da Rasuwar Shi

Bayan sun yi addu’a ga Allah, Ibrahim (A.S) da Hajara sun samu wani yaro da suka sa masa suna Ismail (Isma’il). Wasu malaman sun ce Ibrahim (A.S) ya kasance shekara 86 a lokacin haifuwar Isma’il (A.S).

Ba’a dade ba sai Ibrahim (A.S) ya nemi matarsa Hajar da ta dauko danta Ismail (A.S) duk suka yi tafiya mai nisa, suka isa jeji babu abinci, ‘ya’yan itace da ruwa. Sai Annabi Ibrahim (A.S) ya bar su a cikin jeji da abinci da ruwa wanda suka zo da su.

Lokacin da Ibrahim (A.S) zai tafi sai matarsa Hajar ta tambaye shi: “Shin Allah ne ya umarce ka da ka dauki matakin?” Ya ce: “Na’am.” Sai ta ce masa: “Ba za mu samun damuwa ba, tunda Allah (S.W.T) wanda ya umurce ka yana tare da mu.”

Abincin Hajar da Ismail ba a jima ba suka ƙare, Hajira tayi kishirwa sosai jariri yana kuka. Ta yi ta gudu tsakanin tsaunukan Al-Safa da Al-Marwa sau 7 don neman ruwa da abinci. Sai ta ji wata murya, sai Mala’ika Jibreelu ya bayyana yana buga kafarsa a kasa mai yashi domin ta kawo ruwa. Hajar ta tattara ruwan, ana kiran rafin da sunan “Zamzam”, tun daga wannan rana musulmin da suke aikin hajji suke shan wannan ruwa mai tsarki.

Ba a jima ba Hajar da Isma’il (A.S) suka sami duk abincin da abin sha da suke bukata. Sai Allah (s.w.t) ya aika matafiya zuwa Makka, sai suka ga Hajira da danta, suka tambaye su ko za su iya shiga? Suka yarda, sai matafiya suka zama mazauna kewayen ruwan zam zam.

Bayan wasu lokuta masu tsawo da sauran abubuwan suka wakana tsakanin annabi Ibrahim da dansa Isma’il, sai Allah (S.W.T) ya baiwa Ismail (A.S) aikin Annabci. Don haka ya jagoranci mutanen Amalika a Yaman. Kamar yadda wasu majiyoyi suka ruwaito Isma’il (A.S) ya rayu da wannan al’umma tsawon shekaru hamsin yana isar musu da sako da umarni na Ubangiji. Wasu daga cikinsu sun yi imani da shi amma wasu sun dage a kan kafirci da shirka.

Allah ya fada a cikin Alqur’ani game da Annabcin Isma’il (A.S.):

Kuma ka ambaci Isma'ĩla a cikin Littafi (Alƙur'ãni). Lalle ne! Kuma ya kasance mai gaskiya ga abin da ya yi alkawari, kuma ya kasance Manzo, kuma Annabi. Kuma ya kasance yana umurtar iyalansa da mutanensa da yin Sallah da zakka, kuma Ubangijinsa Ya yarda da shi.

– (Suratul Maryam 19:54 da 55).

Wafatin Isma’il (A.S):

Ismail (A.S) ya rayu shekaru 130 ko 137 a duniya. lokacin da ya rasu. An ruwaito cewa yana da ‘ya’ya maza 12. Kamar yadda wasu majiyoyi suka ruwaito, Isma’il (A.S) ya rayu a Makkah har ya rasu. An binne Ismail (A.S) tare da mahaifiyarsa Hajar a kusa da Kabaa a cikin Masallacin Harami, kamar yadda majiyoyi daban-daban suka bayyana.

Allah (S.W.T) shine mafi sani.