Tarihin Sheikh Abubakar Gero Argungu
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2021/12/image_editor_output_image-2091916255-16405250426141930288160.jpg?resize=691%2C470&ssl=1)
Sheikh Abubakar Gero Argungu, wanda shahararren malamin addinin Muslunci ne na kungiyar Izala, wato Jama’atu Izalatul Bid’a Wa’ikamatus-sunnah (JIBWS).
Kamar yanda mutane suka sani, ko suke ji ana kiran shi, (Abubakar Gero Argungu), garin Argungu wanda yake a cikin jihar Kebbi dake Arewacin Najeriya shine garin da malamin addinin musuluncin ya fito.
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2021/12/images1976511690.jpg?resize=512%2C288&ssl=1)
Sheikh Gero Argungu, sannannen malami wanda har yau yana yin wa’azi na addinin musulunci a ciki fa wajen Najeriya, musamman a ƙasashen Afrika irin su; Jamhuriyar Niger, Ghana, Kamaru, Chadi, Benin sauran wasu ƙasashen da mu iya ambatawa ba.
Har yau Sheikh Gero Argungu shi ne sakataren kungiyar na kasa a halin yanzu na daya daga cikin fitattun kungiyar addini a Najeriya, wacce muka ambata a samu wato IZALA.
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2021/12/image_editor_output_image-2091916255-16405250426141930288160.jpg?resize=512%2C405&ssl=1)
Shugaban wannan kungiya na kasa wani fitaccen malamin addinin musulunci ne a Najeriya mai suna Sheikh Abdullahi Bala Lau.
Kungiyar addini ta yi suna sosai a yankin arewacin Najeriya. Makasudi da makasudin wannan kungiya shine kawai inganta addinin musulunci.