Addini
Misalin Mutanen Annabi Salih A.S, Samudawa [Thamud]
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2023/10/image_editor_output_image447195112-1696627920251-jpg.webp?resize=720%2C370&ssl=1)
Bayan halakar mutanen Adawa [Ad], kabilar Samudawa suka biyo bayan suka gaje su da mulki da daukaka. Mutanen Samudawa sun fada a cikin bautar gumaka.
Yayin da dukiyarsu ta ƙaru, haka ma, mugayen ayyukansu suka ƙaru, yayin da nagartansu ta ragu a bangare ɗaya.
Kamar mutanen Adawa, Samudawa sun gina manya-manyan gine-gine a kan filaye kuma suka sassaƙa kyawawan gidaje daga cikin tuddai na duwatsu. Zalunci da hanci sun zama ruwan dare yayin da mugayen mutane ke mulkin ƙasar.