Addini

Labarin Annabi Ibrahim A.S Da Dangin Shi

Wasu daga cikin Ahlul Kitabi sun bayyana cewa sunansa Ibrahim Ibn Tarikh, Ibn Nahur, Ibn Sarough, Ibn Raghu, Ibn Faligh, Ibn Aher, Ibn Shalih, Ibn Arfghshand, Ibn Sam, Ibn Nuhu.

Suka ce a lokacin Tarikh yana da shekara saba’in da biyar, ya haifi Ibrahim, Nahor (Nohour) da Haran. Haran yana da ɗa mai suna Lutu (Lutu). Sun kuma ce Ibrahim ɗan tsakiya ne kuma Haran ya mutu a zamanin mahaifinsa a ƙasar da aka haife shi, ƙasar Kaldiyawa (Al-Kaldanieen), wanda kuma ake kira Babila.

A lokacin ne wasu mutane na bauta wa gumaka na dutse da na itace; wasu suna bauta wa duniyoyi, taurari, rana da wata; Wasu kuma suna bauta wa sarakunansu da masu mulki.

An Annabi haifi Ibrahim A.S a cikin wannan yanayi, cikin iyali na zamanin da wadannan ba Allah suke bauta wa ba. Shugaban iyali a cikin dangin Annabi Ibrahim ba ma kawai bautar gumaka yake ba, har ma ya kasance wanda baya son Allah gaba ɗaya, kuma ya kasance yana yin gumaka da hannunsa.

Wasu labarai sun yi da’awar cewa mahaifin Annabi Ibrahim ya mutu kafin haihuwarsa, wani kawun shine shi Annabi Ibrahim ya kira uba, wanda ya rene shi. Wasu hadisai sun ce mahaifin shi yana raye har ya girmia, kuma ana kiran shi da sunan Azer.

A cikin wadannan dangin aka haifi Annabi Ibrahim, an ƙaddara shi ya tsaya tsayin daka wajen gaba ko kiyayya da dangin shi da dukan tsarin al’ummar shi na bauta wa wanin Allah.

A taqaice dai ya tsaya tsayin daka wajen adawa da duk wani nau’in shirka na mutanen dangin shi da al’ummar shi da ke bautar gumaka.

Nassosin Alkur’ani:

Abubuwan da suka shafi Alqur’ani na wannan labarin:

Suratul Baqarah aya ta 6:83

Sura ta 4: aya ta 163

Sura ta 14: aya ta 35

Sura ta 60: aya ta 4

Sura ta 21: aya ta 51

Sura ta 21: aya ta 52

Sura ta 3: aya ta 65