Addini

Hadisi Akan Tuhajjud: Awf Yayi Sallar Dare Tare Da Manzon Allah

Awf bn Malik ya ruwaito cewa: “Na tsaya tare da Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, don yin salla da dare (Tuhajjud). Sai Annabi ya fara karanta Suratul Baqarah ba zai wuce ta wata ayar rahama ba sai dai ya roke ta, kuma bai wuce ayar azaba ba sai dai ya nemi tsari daga gare ta. Sa’an nan kuma, Annabi ya yi ruku’u har tsawon lokacin da ya tsaya, yana cewa a cikin ruku’unsa, “Tsarki ya tabbata a gare shi, da mulki, da girma da daukaka.” Annabi ya yi sujjada matukar ya tsaya yana fadin haka a cikin sujjadarsa. Sai Annabi ya fara karanta suratul Ali ‘Imran sannan ya karanta wata sura da wata.

Source: Sunan Abi Dāwud 873

Daraja: Sahih ( ingantacce) kamar yadda Al-Nawawi ya fada

عَنْ عَوْفِ بْنِ مَالِكٍ الْأَشْجَعِيِّ قَالَ قُمْتُ مَعَ رَسُولِ اللَّهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ لَيْلَةً فَقَامَ فَقَرَأَ سُورَةَ الْبَقَرَةِ لَا يَمُرُّ بِآيَةِ رَحْمَةٍ إِلَّا وَقَفَ فَسَأَلَ وَلَا يَمُرُّ بِآيَةِ عَذَابٍ إِلَّا وَقَفَ فَتَعَوَّذَ قَالَ ثُمَّ رَكَعَ بِقَدْرِ قِيَامِهِ يَقُولُ فِي رُكُوعِهِ سُبْحَانَ ذِي الْجَبَرُوتِ وَالْمَلَكُوتِ وَالْكِبْرِيَاءِ وَالْعَظَمَةِ ثُمَّ سَجَدَ بِقَدْرِ قِيَامِهِ ثُمَّ قَالَ فِي سُجودِهِ مِثْلَ ذَلِكَ ثُمَّ قَامَ فَقَرَأَ بِآلِ عِمْرَانَ ثُمَّ قَرَسُ