Addini

Ƙiyayyar Kafirai Ga Annabi Salih A.S

Da farko mutanen Samudawa sun yi mamaki matuka a lokacin da rakumar ta fito daga duwatsu. Rakuma ce mai albarka, nononta ya isa ga dubban maza da mata da yara.

Idan ta kwana a wuri, sauran dabbobi suna kauracewa wurin. Don haka ya tabbata cewa ba rakuma ce kamar sauran rakuma ba, amma daya daga cikin ayoyin Allah ce. Ta rayu a cikin mutanen Annabi Salih A.S, wasu daga cikinsu sun yi imani da Allah yayin da mafi rinjaye suka ci gaba da taurin kai da kafirci.

Kiyayyarsu ga Salih ta koma ga rakumar nan mai albarka, suka koma kan ta. Sai kafirai suka kulla makirci akan rakumar, suka kulla makirci a asirce.

Annabi Salih A.S ya ji tsoron kada su kashe rakumar, sai ya gargade su cewa: “Ya ku mutanena! Wannan rakumar Allah aya ce a gare ku, ku barta ta ci a cikin ƙasar Allah, kuma kada ku shafe ta da wani sharri, kar azaba makusanciya ta same ku.” Ayah 11:64

Bayan wannan gargadin, mutanen Annabi Salih S.A sun bar rakumar ta yi kiwo tana sha, amma a cikin zukatansu sun kyamaci hakan. Sai dai bayyanar mu’ujizar ta rakumar ta musamman yasa mutane da yawa suka zama mabiyan Salih A.S, kuma suka yi imani da Allah.

Nassosin Alkur’ani:

Abubuwan da suka shafi Alqur’ani na wannan labarin.

Surat 7: aya ta 73

Surat 7: aya ta 75