Siyasa
Abba Yusuf Na NNPP Yayi Nasara A Kolin Najeriya
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2024/01/image_editor_output_image-738386941-1705019204747.jpg?resize=616%2C349&ssl=1)
Kotun koli ta tabbatar da Alhaji Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP a matsayin zababben gwamnan jihar Kano.
Nasarar Yusuf a Zaben Gwamna a 2023 ta samu kalubalantar Jam’iyyar APC da dan takararta na Gwamna a Jihar Kano, Alhaji Nasiru Yusuf Gawuna.
A baya kotun daukaka kara ta soke nasarar Yusuf a zaben.