Wata Mata Ta Nemi Kotu Ta Raba Auren Su Akan Rashin Samun Gamsuwa Akan Gado Daga Mijinta

Wata matar aure a karamar hukumar Bwari a babban birnin tarayya Abuja ta maka mijinta kara a wata kotun yankin da ke zamanta a yankin saboda rashin gamsuwar aure akan gado daga mijinta.

Matar mai suna Baraka Abdullahi mai shekaru 23, ta zargi mijinta Bello Abdullahi da rashin zama tare da ita, da kuma rashin samun gamsuwa a lokacin da ya shige lokacin na karshe.

Matar ta shaida wa kotun cewa bayan auren su kimanin shekaru biyu da suka wuce, mijin nata ya kai ta jihar sa ta Kano, ya bar ta a can karkashin kulawar iyayen sa, yayin da ya ci gaba da zama a Abuja inda yake kasuwanci. Ta yi korafin cewa mijin da ke da wata mata a gida daya da ita ya kan ziyarce su bayan kusan watanni uku ba ya nan.

Ta lura cewa duk da cewa ya biya mata dukkan bukatunta na ciyarwa, amma ta yi jayayya cewa mijin bai taba gamsar da ita ba idan aka zo batun kwanciya, don haka tana bukatar saki.

Wanda ake karan ya amince ya dade da zama saboda yanayin kasuwancin sa, wanda a cewar sa, ba zai iya amincewa da wani ba, yayin da ya musanta hakan na gamsuwar aure, kuma ya zarge ta da cewa ba ta taba fadin haka ba.

Alkalin kotun, Abdurrahman Ibrahim, ya amince da bukatar mijin na neman a yi sulhu ta hanyar kebe kwanaki 10, yayin da ya dage sauraron karar zuwa ranar 10 ga watan Fabrairu.