Al'umma
Tsahon Ma’aikacin Gidan Radiyon VOA Hausa, Kabiru Usman Fagge Ya Rasu
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2023/12/image_editor_output_image-1558479123-1702755466797-jpg.webp?resize=224%2C141&ssl=1)
Tsohon ma’aikacin gidan rediyon VOA Hausa, Amurka, Alhaji Kabiru Usman Fagge ya rasu a a kasar Amurka bayan yayi fama da rashin a kasar, Washintan DC.
An haifi Mallam Kabiru Usman Fagge ne a jihar Kano, Najeriya a ranar 12 ga watan Satumban shekarar 1946, kimanin shekaru 77 da suka gabata.
A shekarar Mallam Fagge, a 1956 ya shiga makarantar farko, Firamare ta yankin Fagge a jihar kano, sannan kuma a shekarar 1969 ya kamala karatun gaba ga firamare. Daga bisani ya zarce zuwa Kolejin Horas da Malamai ta Bichi inda ya shekara uku a wannan fanni.
Bugu da ƙari, Usman Fagge ya kammala a Kolejin horas da malamai ta Kano, KTC a shekarar 1970, inda ya sami takardar shaidar koyarwa mai daraja ta biyu (Grade 2).
Ya bar duniya yana shekaru 77.