Al'umma

Tarihin Rayuwar Muhammadu Bello Kagara

Muhammadu Bello Kagara, wanda aka haifa kuma ya rayu a (1890 – 1971) malami ne, marubuci kuma ɗan sarauta. Ya rubuta sanannen littafin novel mai suna Gandoki, novel din rubutun hannu ne da aka rubuta yayin gasar ofishin adabi da Rupert East ya shirya a shekarar 1933. Littafin nasa Ganɗoki an ɗauke shi a matsayin littafi na ɗaya ko na biyu da za a buga a ɗaukacin Arewacin Najeriya, na farko ko na biyu shi ne littafin Ruwan Bagaja na Abubakar Imam.

An haifi Kagara ga iyalan Alkali (babban alkalin) na Kagara, wanda ake kira Shehu Usmanu. Lokacin da yake karami, iyayensa sun gudu daga Kontagora tare da Sarkin Sudan Nagwamatse don hana kansu mamaye sojojin Ingila, domin su kasance karkashinsu.

Kagara ya taba zama dalibi a makarantar Nassarawa, daga baya bayan kammala karatunsa, ya karantar da karatun addinin Musulunci da na Larabci a kwalejin Katsina (Barewa College a yanzu) har zuwa shekarar 1945. Kafin ya shiga kwalejin, ya koyar a Makarantar Lardin Zariya (Alhudahuda College).

Daga baya kuma a cikin aikinsa aka ba shi sarautar mahaifinsa, wanda aka fi sani da wali ko Daneji na Katsina, ya zama babban alkali na gargajiya “Alkali” a karamar hukumar Katsina.