Al'umma
Tarihin Mallam Ayuba Musa Lukuwa
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2021/12/image_editor_output_image1050918983-16405320660031701614148.jpg?resize=372%2C394&ssl=1)
Mallam Musa Lukuwa, wanda cikakken sunan shi shine; Ayuba Musa Lukuwa, shahararren malamin addinin Musulunci ne dake zaune a jihar Sakkwato dake Arewacin Nigeriya.
Mallam Musa ya karantar da dalibai ilimomin addinin musulunci da dama a cikin Sakkwato da kewayenta, wanda daga cikin daliban Mallam Musa akwai Mallam Murtala Bello Assada.
Mallam Musa Lukuwa, mutum ne wanda yayi kaurin suna a wajen gwamnatin jihar Sakkwato da wadansu sarakuna a jihar, musamman idan azo fannonin da suka shafi addinin musulunci.
Idan dai ba’a manta ba, barkewar cutar Korona Bayiros (COVID-19) ta sanya malamin da hukumomi takun saka musamman saboda wasu dokoki da ka shinfada game da tarurrukan addinin musulunci kamar sallah da wa’azi.
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2021/12/images652499033.jpg?resize=480%2C480&ssl=1)