Al'umma
Kudin Hayar Gidaje A Abuja Sun Yi Tashin Gwaurayen Zabi
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2024/02/Screenshot_2024-02-24-10-07-45-140.jpg?resize=717%2C470&ssl=1)
Mazauna babban birnin tarayya, FCT, Abuja, Najeriya basu da wani abin dogaro kan tsadar hayar gidaje da ke babban birnin kasar.
Hakan na faruwa ne yayin da wasu masu gidaje a babban birnin kasar suka dora alhakin tsadar kayan gini a kan lamarin.
Wasu masu gidaje sun koka da cewa yayin da kudin gina sabon gini a Abuja ya haura sama da kashi 200 idan aka kwatanta da yadda yake a da a watannin baya, kula da tsofaffin gidajen kuma ba karamin aiki ba ne.
A cewarsu, kayayyakin da ake amfani da su wajen gine-gine, da rayawa, da gyaran gine-gine basu da araha a Najeriya.
Ginin yana tafiya ne ta hanyar kulawa a tsawon rayuwarsa kuma wasu masu gidaje sun ce ba aiki mai sauƙi ba ne.