Al'umma

“Ina Ji Kamar Cikin Aljanna Na Ke” – Inji Wani Matashi Da Ya Auri Mata 2 Lokaci Guda

Wani matashi mai suna Umar Sani da ya auri mata biyu a rana guda a garin Minna na jihar Neja, ya ce yana ji kamar yana aljanna.

Umar, wanda ya auri Safina da Maryam a ranar Juma’a, ya shaida wa wata jarida ta yanar gizo da ke Minna, Tsalle Dayya, cewa “Ina ji kamar an ba ni fili a aljanna, ina godiya ga Allah matuka.

“Na gode wa Allah da farin ciki na auri auran biyu. Dukansu suna da fahimta, kuma ina godiya da hakan.

“Mutane da yawa sun yi tunanin cewa za a sami matsala daga ɗayansu, amma Allah cikin hikimarsa, ya sa abubuwa su zama cikakku.”

Umar ya bayyana cewa ya yanke shawarar ne saboda asalin danginsa da ya yi auren mata fiye da daya.

“Tun ina dan shekara 10, na ga mahaifina yana da mata hudu kuma na ga yadda suke zaman lafiya. Na yi wa kaina alkawari zan auri mata fiye da daya idan na samu hanya, ko in yi aure uku ko hudu a rana guda”.

Ko da yake ya ce iyayensa sun yi mamakin shawarar, amma ba su hana shi cika burinsa ba.

“Iyayena sun yi mamaki domin ko mahaifina bai auri mata biyu a rana daya ba. Amma ba su yi adawa da shi ba. Abu mafi muhimmanci a gare mu a yanzu shi ne mu samu gida lafiya,” inji shi.