Al'umma
Hikimar Ɗan Gidan Yari
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2023/06/FB_IMG_1686655367613.jpg?resize=720%2C470&ssl=1)
Wani tsoho Mmanomi ya rubuta wa ɗansa wasika da ke kurkuku:
“Ɗana, bana iya shuka Dankali, don ba zan iya nome gonar da kaina ba, nasan idan kana nan zaka ka taimake ni”.
Ɗan ya rubutowa mahaifin shi amsa:
“Baba kar ka yi tunanin noman filin domin a nan ne na binne duk kudin da na sata.”
‘Yan sanda suna karanta wasikar sai washegari aka nome filin gaba daya ana neman kudin, amma ba a ga komai ba.
Washe gari ɗan ya sake rubutawa mahaifinsa wata wasikar:
‘Yanzu baba zaka iya shuka dankalin ka, wannan shine mafi kyawun da zan iya yi maka daga nan. ‘