Al'umma

Aziza Adam Mandeel: Matar Ta Lashe Gasar Kyau Ta Khartoum A 1958

Kakanta wani Bayahude dan Morocco ne wanda ya kasance yana tafiya Sudan don kasuwanci (sayar da lu’u-lu’u da siliki). Daga baya ya musulunta ya zauna a kasar Sudan, ya zama abokin shugaban kasar Sudan AlMahdy, wanda ya ba shi shawarar a matsayin namiji da ya auri ‘yar daya daga cikin manyan sarakunan kasar Sham, ya kuma haifi ‘ya’ya 6 daya daga cikin su shi ne Adam (mahaifin Aziza).

Aziza ta shahara da kyawunta kuma ta kasance cikin wakokin Sudan da dama daga shahararrun mawaka a wancan lokacin irin su Hajj Mohamed ahmed Sorror da Ebied AbdelRahman.

Yanzu tana da shekaru 84 kuma tana zaune a Sudan.