Wasanni
Yan Najeriya 6 Da Aka Taɓa Zaɓa A Takarar Gwarzon Ɗan Kwallon Duniya Na Ballon d’Or
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2022/02/fb_img_1643707933488846624030.jpg?resize=552%2C470&ssl=1)
‘Yan Najeriya shida ne aka zaba a matsayin gwarzon dan kwallon duniya na Ballon d’Or.
Kanu Nwankwo ya zo na 11 a takarar matsayin gwarzon dan wasan kwallon kafa na duniya a shekarar 1996- wanda shine matsayi mafi girma na dan wasan Najeriya.
Finidi George ya kasance a matsayi na 21 a cikin 1995.
Victor Ikpeba ya kasance a matsayi na 32 a cikin 1997.
An zabi Daniel Amokachi a shekarar 1995 amma bai samu kuri’a ba.
An zabi Austin Okocha a shekarar 1995 da 1996 amma bai samu kuri’a ba sau biyu.
An zabi Sunday Oliseh a shekarar 1998 amma bai samu kuri’a ba.