Wasanni
Yadda Ake Fitar Da Wanda Yayi Nasara A Wasa Da Ta Tashi 0-0 Kafin Shigo Da ‘Bugun Finareti’
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2023/03/FB_IMG_1680001266666.jpg?resize=719%2C470&ssl=1)
Kafin gabatar da bugun daga kai sai mai tsaron raga (Finareti) a wasan kwallon kafa, sake buga wasan na daya daga cikin hanyoyin da aka saba amfani da su wajen tantance wanda ya yi nasara a wasan da aka tashi canjaras (0-0 ko 1-1).
An buga wasan karshe na gasar Euro 1968 tsakanin Italiya da Yugoslavia sau biyu- wasan farko ya tashi 1-1 yayin da Italiya ta sake samun nasara da ci 2-0 a wasa ta biyu.
An buga wasan karshe na AFCON 1974 tsakanin Zaire da Zambia sau biyu- wasan farko ya tashi 2-2 yayin da Zaire ya sake lashe gasar da ci 2-0 a bugu na biyu.