Tarihin Kungiyar Kwallon Ƙafa ‘Shooting Stars SC’ Ta Ibadan, Jihar Oyo
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2023/08/FB_IMG_1691957393143.jpg?resize=719%2C393&ssl=1)
Shooting Stars SC, wacce aka kafa a shekarun 1950, tana daya daga cikin wadanda suka kafa gasar firimiya ta Najeriya a shekarar 1972. A da ana kiran su da WNDC Ibadan.
Sun lashe gasar Firimiyar Najeriya sau 5, sannan sun lashe kofin FA na Najeriya sau 8.
Sun lashe gasar cin kofin nahiyar Afirka a shekarar 1976, inda suka zama kulob na farko a Najeriya da ya lashe kofin duniya.
Sau biyu sun kare a mataki na biyu a gasar cin kofin zakarun nahiyar Afirka ta CAF, inda suka yi rashin nasara a hannun Zamalek na Masar a duka lokutan biyun. Sun yi rashin nasara da ci 3-0 a jumulla a wasan karshe na 1984 kuma sun sha kashi 5-4 a bugun fanariti a wasan karshe na 1996.
Fitattun ‘yan wasan da suka taka leda a kungiyar sun hada da: Segun Odegbami, Muda Lawal, Felix Owolabi, Rashidi Yekini, Best Ogedegbe, Taiwo Ogunjobi da Ajibade Babalade.