Wasanni

N’Golo Kante Na Chelsea Ya Bar Sansanin Faransa

N’Golo Kante na Chelsea ya bar sansanin yan wasan kasar Faransa ranar Talata saboda wasu dalilai na kashin kan shi.

RMC Sports ta ruwaito cewa Kante dole ne ya ‘tashi’ saboda wasu dalilai na kashin kan shi gabanin wasan sada zumuntar Faransa da Ivory Coast ranar Juma’a.

Dan wasan mai shekaru 30 zai hadu da Les Bleus a wasan da za su buga da Ivory Coast da Afrika ta Kudu.

Sai dai bayan da aka kulla alaka da kungiyar kwallon kafa ta kasar a farkon makon nan, dan wasan ya janye daga wasan na wani dan lokaci.

Babu tabbas ko Kante zai koma sansanin Didier Deschamps na wasannin biyu.

A halin yanzu, Faransa na iya kasancewa ba tare da Presnel Kimpembe, Hugo Lloris da Mike Maignan ba a wasannin da ke tafe saboda rauni.

A ranar Laraba ne ‘yan wasan uku za su dawo.