Dan Kwallon Afrika Da Ya Fi Kowa Buga Wasanni A Premier League
Kolo Toure shi ne dan wasan Afrika da ya fi kowa buga wasanni a gasar Premier (353): Arsenal (wasu 225), Manchester City (wasu 82) da Liverpool (wasu 46).
Bayan ya lashe gasar da Arsenal a 2003/04 da kuma Manchester City a 2011/12, ya kusa zama dan wasa na farko da ya lashe gasar tare da kungiyoyi daban-daban uku a lokacin da ya kare a matsayi na biyu da Liverpool a 2013/14 maki biyu kacal a kasa da Manchester City da ta lashe gasar. .
Ya lashe kofunan lig sau biyu ba tare da an doke shi ba a rayuwarsa – Premier da Arsenal a 2003/04 da kuma gasar firimiya ta Scotland da Celtic a 2016/17.
Ya lashe gasar cin kofin Afrika da Ivory Coast a shekarar 2015, kuma shi ne dan wasa na biyu da ya fi yawan buga wa kasar wasanni 120.
A halin yanzu shi ne kocin kungiyar farko a Leicester City sannan kuma memba ne na masu horar da ‘yan wasan kasar Ivory Coast.
Ya cika shekaru 41 a 2022.