Ahmed Musa: Wasu Daga Cikin Nasarorin Shi A Kwallon Kafa

Ahmed Musa ya kasance daya daga cikin fitattun ‘yan wasan Super Eagles a shekaru goma da suka gabata, shi ne dan wasan da ya fi zura kwallo a raga a gasar cin kofin duniya ta FIFA da kwallaye 4.

Shi ne kuma dan wasan Super Eagles da ya fi taka leda a wasanni 108 kuma yana daya daga cikin ‘yan wasan kwallon kafa na kasa da kasa a duniya.

A wajen wasan kwallon kafa, mutum ne mai taimakon jama’a kuma mutum ne mai tausayin zuciya, yayi ayyuka masu yawa ga mutane da kuma ’yan wasan kwallon kafa na Najeriya.

Takaitacciyar nasarorin da ya samu kawo yanzu:

CSKA

Premier League na Rasha: 2012, 2013, 2014, 2015 da 2016

Kofin Rasha: 2012 da 2013

Gasar cin kofin Rasha: 2013 da 2014

Al-Nassr

Saudi Professional League: 2018 da 2019
Saudi Super Cup: 2019

Najeriya U20

Gasar Matasan Afirka: 2011

Najeriya

WAFU Nations Cup: 2010
Gasar Cin Kofin Afirka: 2013

Sauransu

Gasar Firimiyar Najeriya: 2009 da 2010

A cikin jerin 33 mafi kyawun ‘yan wasan ƙwallon ƙafa na gasar zakarun Rasha: 2012 da 2013

Gasar Cin Kofin Rasha: 2012–2013

Kungiyar CAF ta Shekara: 2014.