Ahmed Musa ya kasance daya daga cikin fitattun ‘yan wasan Super Eagles a shekaru goma da suka gabata, shi ne dan wasan da ya fi zura kwallo a raga a gasar cin kofin duniya ta FIFA da kwallaye 4.
Shi ne kuma dan wasan Super Eagles da ya fi taka leda a wasanni 108 kuma yana daya daga cikin ‘yan wasan kwallon kafa na kasa da kasa a duniya.
A wajen wasan kwallon kafa, mutum ne mai taimakon jama’a kuma mutum ne mai tausayin zuciya, yayi ayyuka masu yawa ga mutane da kuma ’yan wasan kwallon kafa na Najeriya.
Takaitacciyar nasarorin da ya samu kawo yanzu:
CSKA
Premier League na Rasha: 2012, 2013, 2014, 2015 da 2016
Kofin Rasha: 2012 da 2013
Gasar cin kofin Rasha: 2013 da 2014
Al-Nassr
Saudi Professional League: 2018 da 2019
Saudi Super Cup: 2019
Najeriya U20
Gasar Matasan Afirka: 2011
Najeriya
WAFU Nations Cup: 2010
Gasar Cin Kofin Afirka: 2013
Sauransu
Gasar Firimiyar Najeriya: 2009 da 2010
A cikin jerin 33 mafi kyawun ‘yan wasan ƙwallon ƙafa na gasar zakarun Rasha: 2012 da 2013
Gasar Cin Kofin Rasha: 2012–2013
Kungiyar CAF ta Shekara: 2014.