Wasanni

Ɗan Najeriya Na Farko Da Ya Fara Buga Wasa A Gasar Premier League Ta Ingila

Efan Ekoku shi ne dan Najeriya na farko da ya fara buga gasar Premier ta Ingila.

Shi ne dan wasan Najeriya na uku a kan gaba wajen zura kwallaye a gasar Premier da kwallaye 52, bayan Kanu Nwankwo mai kwallaye (54) da Yakubu Aiyegbeni da ke da kwalleye (95).

A watan Satumban 1993, ya zama dan wasan Najeriya na farko da ya ci Hattrick a gasar Premier a karawar da Norwich City ta doke Everton da ci 5-1 a Goodison Park. A hakika ya zura kwallaye hudu a wasan.

A matakin kasa da kasa, ya buga wa tawagar kwallon kafar Najeriya wasanni shida.

Bayan da yayi ritaya, Ekoku yayi aiki a matsayin mai sharhi, kwararre da kuma manazarcin wasa.

An shigar da shi cikin Babban Birnin Norwich a cikin shekarar 2012.