Labarai

‘Yan Yawayen Abzinawa Sun Yi Ikirarin Ƙwace Garin Arewacin Mali Bayan Makonni Ana Gwabza Faɗa

‘Yan tawayen Abzinawa a arewacin Mali sun yi ikirarin kwace wani sansanin soji da ofisoshinsu a garin Bourem bayan shafe makwanni ana gwabzawa da sojojin kasar da sojojin haya na Wagner, inda suka yi barazanar warware yarjejeniyar zaman lafiya da aka cimma a shekara ta 2015.

Kame Bourem da ke tsakanin tsoffin garuruwan Gao da Timbuktu a ranar Talata da kawancen ‘yan tawayen Abzinawa da ake kira Coordination of Azawad Movements (CMA) ya zo ne a daidai lokacin da sojoji suka hada karfi da karfe a juyin mulki guda biyu a 2020 da 2021 tare da fatattakar sojojin Faransa da Majalisar Dinkin Duniya da tawagar wanzar da zaman lafiya ta MINUSMA.

Kakakin CMA Mohamed Elmaouloud Ramadane ya ce “Na tabbatar da cewa CMA ta karbe iko da sansanin da misalin karfe 10 na safe bayan kazamin fada.” Ya ce an samu asarar rayuka amma har yanzu bai san adadin wadanda suka mutu ba.

Mai magana da yawun sojojin Mali bai mayar da martani nan take ba kan bukatar yin sharhi.

Mahamoud Ould Mety mazaunin yankin ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters ta wayar tarho cewa “kungiyoyi masu dauke da makamai da ba a san ko su wane ne ba sun kewaye sansanin kuma suka zagaya cikin garin.”

“Amma jirgin ya mayar da martani a kansu. Muna iya jin karin harbe-harbe, FAMA (Rundunar Sojin Mali) suna ko’ina cikin garin a adadi,” in ji shi.

Yankin – shi ne mahaifar ‘yan tawaye masu dauke da makamai da suka mamaye yankin Sahel – an sake samun barkewar tashin hankali a cikin ‘yan makonnin da suka gabata, sakamakon janyewar dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya wanda ya taimaka wajen wanzar da zaman lafiya.

Madogara:

https://www.aljazeera.com/news/2023/9/12/tuareg-rebels-claim-control-of-northern-mali-town-after-weeks-of-fighting