Labarai
Yadda Jirgin Kasa Ya Darkake Wata Mota Da Mutanen Da Ke Ciki A Abuja
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2022/12/Screenshot_2022-12-15-15-35-08-129.jpg?resize=716%2C407&ssl=1)
Kwanaki kadan bayan da gwamnatin tarayya ta sanar da dawo da zirga-zirgar jiragen kasa a hanyar Abuja zuwa Kaduna, an samu wani hadari.
Arewa Times ta tattaro cewa motar wacce wata mata ke tuki da har yanzu ba a tantance ba jirgin ya murkushe motar a unguwar Kubwa a Abuja ranar Alhamis.
Bidiyon hadarin ya nuna cewa jirgin ya murkushe wata bakar mota kirar Toyota Camry daga bangaren direban yayin da motar ke tsallaka titin jirgin.
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2022/12/Screenshot_2022-12-15-15-36-12-475.jpg?resize=512%2C322&ssl=1)
Kazalika kakakin hukumar kula da zirga-zirgar jiragen kasa ta Najeriya (NRC), Mahmood Yakoob, ya tabbatar da aukuwar lamarin, amma ya kasa bayar da cikakken bayani har zuwa lokacin hada wannan rahoto.
Har ila yau, ba a iya tabbatar da yanayin direban motar ba tukuna.