Labarai

Wata Mata Ta Bankawa Kanta Wuta Saboda Saurayi A Jigawa

An samu wani mummunan lamari a karamar hukumar Dutse ta jihar Jigawa, inda wata mata mai suna Maryam Aminu ‘yar shekara 35 ta bankawa kanta wuta.

TrackNews ta ruwaito cewa, a cewar Mista Adamu Shehu, jami’in hulda da jama’a na hukumar tsaro ta farin kaya (NSCDC) a jihar, lamarin ya faru ne da misalin karfe 2:00 na safiyar ranar Alhamis a unguwar Gindin Dinya da ke Dutse.

An tattaro cewa matar ta zargi saurayin nata da yi mata magudi, lamarin da yasa ta fusata.

“Duk da cewa har yanzu ba a san musabbabin faruwar lamarin ba, ana zargin tana da alaka ne da wani saurayin ta mai shekaru 40, mai suna Ibrahim Haruna.

“Matar ta samu ciwon konewar sosai, yanzu haka tana samun kulawar likitoci a babban asibitin Dutse,” inji shi.

Wani ganau mai suna Muhammad Yusif ya bayyana cewa ta fusata ne a lokacin da ta samu labarin cewa saurayinta ya je ganin wata mata.

“Ma’aikaciyar lalata ce mai kishi da ke zaune a unguwar.

“Matar ta yi zargin cewa saurayinta ya je ganin wata mata kuma ya yi yunkurin kashe kansa.”

Cikin zafin nama ance ta yi amfani da fetur wajen cinna wa kanta wuta.

An yi sa’a wasu mutanen unguwar sun yi nasarar kashe gobarar tare da ceto wanda abin ya shafa. Sai dai rahotanni sun ce ta samu munanan konewa inda aka garzaya da ita asibiti domin kula da lafiyarta.

Binciken farko da hukumar NSCDC ta gudanar ya nuna cewa lallai wadda aka kashe ta yi amfani da fetur wajen cinna wa kanta wuta.