Labarai
Shahararren Malamin Addinin Musulunci, Gero Argungu Ya Rasu
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2023/09/Screenshot_20230906-202954_Chrome-jpg.webp?resize=780%2C470&ssl=1)
Shahararren malamin addinin musulunci Sheikh Abubakar Giro Argungu ya rasu.
Sakataren kungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’a wa Iqamatus Sunnah, (JIBWIS), Kabir Muhammad Haruna ya tabbatar da hakan a wani sako da ya wallafa ta shafinsa na Facebook da aka tabbatar a ranar Laraba.
Ya bayyana cewa, malamin ya rasu ne a Birnin Kebbi, jihar Kebbi, bayan gajeruwar rashin lafiya.
“Mu daga Allah muke, kuma zuwa gare Shi muke komawa.
“Sheikh Abubakar Giro Argungu ya rasu.
“Za a yi jana’izar marigayin gobe Alhamis kamar yadda addinin Musulunci ya tanada. Za a sanar da lokacin jana’izar nan gaba kadan,” in ji Sakataren JIBWIS na kasa