Labarai
Haren-Haren Isra’ila Sun Lalata Masallatai 380 A Gaza
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2024/01/image_editor_output_image1857152816-1705011233004.jpg?resize=677%2C390&ssl=1)
A cewar wata sanarwa da ofishin yada labaran Gaza ya fitar, masallatai akalla 380 aka lalata – ciki har da tsofaffi masu shekaru sama da 1,000.
Rugujewar wadannan masallatai ya haifar da bacewar kiran salla daga unguwanni da dama a yankin Zirin Gaza, da kuma dakatar da kararrawar majami’u.
Sanarwar ta kuma yi nuni da cewa, an lalata majami’u uku a hare-haren da sojojin Isra’ila suka kai.
Ofishin yada labarai na kira ga kungiyoyin addini na duniya da su yi Allah wadai da lalata wadannan wuraren ibada.