Gwamnatin Sojan Nijar Ta Umarci Ƴan Sanda Su Kori Jakadan Faransa
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2023/09/download-1.webp?resize=780%2C470&ssl=1)
Rundunar sojan Nijar ta soke kariyar jakadan Faransa tare da umurtar ‘yan sanda da su kore shi daga kasar da ke yammacin Afirka, a cewar wata sanarwa daga gwamnatin mulkin soja.
Sojojin da suka hambarar da shugaban Nijar sama da wata guda sun ba jakadan Faransa Sylvain Itte sa’o’i 48 ya fice daga kasar a makon jiya. Wa’adin ya kare ne a ranar 28 ga watan Agusta ba tare da Faransa ta kira Itte ba.
Gwamnatin Faransa ta ce ba ta amince da masu yunkurin juyin mulkin a matsayin halastattun shugabannin kasar ba, kuma mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Faransa Anne-Claire Legendre ta fada jiya Alhamis cewa jakadan yana nan a wurin duk da barazanar korar da ake yi.
Sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Nijar ta aike a farkon wannan makon kuma kamfanin dillacin labarai na Associated Press ya gani a ranar Alhamis ta ce Itte “ba ya samun gata da kuma kariya daga matsayinsa na ma’aikacin diflomasiyya na ofishin jakadancin.”