Labarai

Masu Zanga-Zangar Dake Kaɗa Tutocin Rasha Zasu Fuskanci Tuhumar Laifin Cin Amanar Ƙasa – Sojoji

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Litinin cewa mutanen da ke baje kolin tutocin kasar Rasha yayin zanga-zangar da ake yi a fadin kasar suna cin amanar kasa kuma za a gurfanar da su a gaban kuliya.

Babban hafsan hafsoshin tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa ne ya bayyana hakan bayan taron majalisar tsaron kasar da shugaba Bola Tinubu ya jagoranta a fadar Aso Rock Villa da ke Abuja. Ya jaddada cewa irin wadannan ayyukan ba su da “tunani” kuma za a dauke su a matsayin laifukan cin amanar kasa.

A ranar 3 ga Agusta, 2024, yayin zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa, an ga wasu masu zanga-zanga a jihar Kano suna daga tutar kasar Rasha. Hotuna da bidiyo sun nuna waɗannan masu zanga-zangar suna rera waƙa a cikin harshen Hausa, “Ba ma son gwamnati mara kyau.” A ranar Litinin ne aka samu labarin irin wannan lamari a Kaduna, inda aka kuma ga masu zanga-zangar suna daga tutocin kasar Rasha suna rera wakar, “Maraba, Rasha; Barka da zuwa Rasha.”

Janar Musa ya ce, “Ga wadancan tutoci, kuma idan ka ga da yawa daga cikinsu, yara ne ake turawa yin hakan. Muna tafe ga wadanda ke daukar nauyinsu. Waɗancan suna tura su ne domin, ka sani, an yi ta folo. Mun gano wadannan wuraren, kuma za mu dauki mataki mai tsanani a kansu.”

Musa ya kara da cewa “Shugaban kasa ya bayyana karara a cikin umarnin da ya ba mu cewa kada mu yarda da duk wanda ke son kawo cikas ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a Najeriya.”

“Muna gargadi a bayyane, kuma shugaban kasar ya kuma ce ya kamata mu isar da wannan: Ba za mu yarda da kowa ba, duk wani mutum da ke dauke da wata tutar kasashen waje a Najeriya.