Al'umma

Muslunci: Labarin Kiristoci Biyu, ‘Isaac Da Jacob’ Da Suka Ɓace A Sahara

Isaac da Jacob yahudawa biyu ne da suka ɓace a Sahara.

A gajiye da kishirwa da yunwa suka iso wani kauyen musulmi.

Isaac ya ce wa Jacob: “Dole ne mu yi kamar cewa mu Musulmi ne don su ba mu abinci.

Jacob ya ce: “Ba zan yi ƙarya ba, zan faɗa musu gaskiya.

Da shigar su kauyen sai mutanen kauyen suka tambayi sunayen su.

Isaac ya ce sunana Abdallah, sai Jacob ya ce: Ni suna na Jacob.

Shugaban ƙauyen ya ce: Ku ɗauki ɗan’uwa Jacob a ba shi abinci da abin sha.

Sannan ya dubi Isaac yana cewa: dan’uwa Abdallah musulmi ne kuma Ramadana ne yanzu, don haka ku sama masa wurin hutawa har zuwa lokacin buda baki (fadi) ya sha ya ci.

#Afirka #Barkwanci