Kamal Aboki: Abin Da Mahaifiyata Ta Fada Min Kafin Dan Uwana Yayi Hatsari

Jama’a da dama sun kadu matuka dangane da hadarin da ya yi sanadin mutuwar wani fitaccen dan wasan barkwanci, Kamal Iliyasu Usman, wanda aka fi sani da Kamal Aboki a Tiktok, Facebook da YouTube.

Matashin mai shekaru 26 dan wasan barkwanci ne kuma mawakin da ake zaton ya je Maiduguri ne domin kaddamar da wani album. A ranar 16 ga watan Janairu yayin da yake kan hanyar shi ta komawa Kano, ya yi mummunan hatsarin mota wanda ya yi sanadin mutuwar shi.

Wani dan uwa ga Kamal Aboki, Usman Iliyasu ya yi zargin cewa mahaifiyarta shi ji wani mummunan abu zai faru a lokacin da Kamal ya ce yana cikin motar a hanyar shi ta zuwa Kano. Ya bayyana abin da mahaifiyar shi ta gaya masa a wata hira da BBC Pidgin.

Ya ce, ‘Kamal ya je Maiduguri ne kwanaki uku da suka wuce don kaddamar da faifan album guda daya, kuma ya shirya komawa Kano a lokacin da wannan abin takaici ya faru. Mahaifiyata ta ce in kira shi, bayan na kira shi da misalin karfe 5 na yamma, ya ce mana yana cikin mota a hanyar shi ta zuwa Kano. Mahaifiyata ta gaya min cewa ta ji ko ta yaya nan da nan. Daga baya sai wani ya kira ni ya fara magana da harshen Kanuri wanda ban gane ba. Daga baya ya tambaye ni ko ina da wanda ke tafiya daga Maiduguri zuwa Kano? Ya sanar dani labarin hatsarin.”