Al'umma
Dalibai 700 Sun Kammala Karatun Haddar Qur’ani A Habasha
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2022/03/97836_4661370623048.jpg?resize=600%2C400&ssl=1)
An gudanar da bikin ne a ranar Asabar a wani kauye da ke yankin Oromia na kasar Habasha (Ethiopia).
Duk wadannan dalibai sun yi karatun haddar darussa a wata cibiyar Musulunci mai suna Zaid bin Thabet.
Wani mai wa’azi dan kasar Habasha Sheikh Amin Abreu ya wallafa hotuna da bidiyo a lokacin da yake halartar bikin, inda ya nuna daliban sun yi layi a cikin rigar kauye suna yawo a kan titunan kauyen domin murnar wannan rana.
![](https://i0.wp.com/arewatimes.com.ng/wp-content/uploads/2022/03/97837_9441567254414.jpg?resize=512%2C341&ssl=1)