Labarai

Burkina Faso, Mali Za Su Marawa Nijar Baya Su Ƙalubanci ECOWAS

Masu mulkin soji na Burkina Faso da Mali sun yi gargadin cewa duk wani tsoma bakin soji kan jagororin juyin mulkin da suka yi a Nijar a makon da ya gabata, za a dauki shi a matsayin ” ayyana yaki” kan kasashen su.

Makwabtan Nijar sun yi wannan gargadin ne a cikin wata sanarwar hadin gwiwa da aka karanta a gidajen yada labaran su na kasar a ranar Litinin, kwanaki bayan shugabannin kasashen yammacin Afirka sun yi barazanar yin amfani da karfi wajen maido da hambararren shugaban Nijar Mohamed Bazoum.

Shugabannin rikon kwarya na Burkina Faso da Mali sun bayyana goyon bayan su ga al’ummar Nijar, wadanda suka yanke shawarar daukar makomar su a hannu tare da daukar cikakken ikon su kafin tarihi.

“Duk wani tsoma bakin soji a kan Nijar zai kasance daidai da shelanta yaki da Burkina Faso da Mali,” sun yi gargadin, tare da kara da cewa irin wannan matakin na iya haifar da “mummunan sakamako” da “ka iya hargitsa yankin gaba daya”.

Hukumomin sojan Burkina Faso da Mali sun kuma ce sun ki aiwatar da takunkumin da aka kakaba wa jama’a da hukumomin Nijar ba bisa ka’ida ba.

Juyin mulkin da aka yi a Jamhuriyar Nijar a ranar 26 ga watan Yuli ya jefa girgizar kasar a yammacin Afirka, lamarin da ya barke tsakanin tsoffin kawancen kasashen yammacin Turai da kuma wasu kasashen yankin.

Jagororin juyin mulkin jamhuriyar Nijar, wadanda suka bayyana Janar Abdourahamane Tchiani, tsohon hafsan tsaron fadar shugaban kasa a matsayin shugaban kasa, sun ce sun hambarar da Bazoum ne saboda rashin shugabanci na gari da rashin gamsuwa da yadda ya magance barazanar tsaro daga kungiyoyin da ke da alaka da al-Qaeda da ISIS (ISIL).