Abinda Dr. Idris Abdul-Aziz Ya Fada Akan Neman Taimakon Allah

Wannan ita ce maganar Sheikh Dr Idris Abdul-Aziz Bauchi ya fada akan neman tsarin Allah da taimakon Shi.

Ba zaka gane mutane suna cikin subha ba, sai a lokacin da wani malami yayi fatawa ta gaskiya wadda suka gaza fahimta.

Abu ne mai sauki a Tauhidi, ba’a daukan hakki da matsayin Allah a bawa Annabi (S.A.W), kamar yadda ba’a daukan na Annabi (S.A.W).

Hakika duk wanda yaje makaranta addini mai tsafta ya san abin da malam ya fada haka ne, sai idan mutum ya jahilci abin.